Yara 51 Sun Ɓace Bayan Mummunan Harin ‘Yan Ta’adda A Borno
Tun da fari, an rawaito cewa wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram/ISWAP ne sun kai hari makarantu da gidaje a ƙauyen, lamarin da ya sa sama da yara 40 suka ɓace ba tare da an san inda suke ba.
Sai dai sabbin bincike da shugabannin al’umma tare da iyalan da abin ya shafa suka gudanar sun nuna cewa adadin yaran da har yanzu ba a gano ba ya ƙaru sosai, abin da ya ƙara jefa al’ummar yankin cikin firgici da alhini.
Mazauna yankin sun bayyana cewa har yanzu iyaye da ‘yan uwa na ci gaba da neman ‘ya’yansu, yayin da ake fargabar cewa wasu daga cikin yaran na iya faɗa hannun ‘yan ta’addan da suka addabi yankunan Arewa maso Gabas.
Rahotanni sun nuna cewa harin ya haddasa tashin hankali a yankin, inda mutane da dama suka tsere daga gidajensu domin neman mafaka a wurare masu tsaro.
Comments
Post a Comment