🚨 LABARIN GAGGAWA: Ɗan El-Rufai a Majalisar Wakilai Ya Fice Daga APC Zuwa ADC

ÆŠan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kuma É—an majalisar wakilai mai wakiltar Kaduna North, Bello El-Rufai, ya fice daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar ADC. 

Rahotanni sun bayyana cewa Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ne ya karanta wasiÆ™ar sauya shekar Bello El-Rufai a zaman majalisar na ranar Alhamis. 

Baya ga Bello El-Rufai, wasu ‘yan majalisa biyu daga jihar Kaduna — Umar Ajilo da Suleiman Richifa — suma sun bar PDP zuwa ADC, yayin da wasu ‘yan majalisa suka koma sabbin jam’iyyu daban-daban. 

Majiyoyi sun ce ‘yan majalisar sun danganta matakin nasu da rikice-rikicen cikin gida da rashin tabbas da ke addabar tsofaffin jam’iyyunsu. 

Sauya shekar Bello El-Rufai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa gabanin zaÉ“en 2027, lamarin da ke Æ™ara girgiza APC musamman a jihar Kaduna. 

Comments

Popular posts from this blog

BREAKING: FG Approves 40% Pay Rise —Non-Academic Staff Left Out

Nigeria’s Ivory Towers in Ruins: An Investigative Look at the Dilapidated State of Nigerian Universities

BREAKING: US Finally Withdraws from WHO