Shugaba Tinubu Ya Yi Ƙaramin Sauyi a Majalisar Ministoci, Edun da Ɗangiwa Sun Bar Muƙamansu
Sanarwar ta fito ne daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), inda ya sanya hannu kan wata takarda da ke bayyana matakin.
A cewar sanarwar, tsohon Ministan Kuɗi kuma Mai Kula da Tattalin Arziƙi, Wale Edun, ya bar muƙaminsa, kuma an umurce shi da ya miƙa ragamar aiki ga Taiwo Oyedele, wanda yanzu aka ɗaga shi zuwa matsayin Ministan Kuɗi kuma Mai Kula da Tattalin Arziki. Kafin wannan naɗin, Oyedele ya kasance Ƙaramin Minista a ma’aikatar.
Haka kuma, an sanar da cewa Ahmed Musa Ɗangiwa zai bar muƙaminsa na Ministan Gidaje da Raya Birane, yayin da aka gabatar da Muttaqha Rabe Darma a matsayin sabon minista a wannan ma’aikata.
Takardar ta kuma umarci dukkanin ministocin da abin ya shafa da su kammala dukkan hanyoyin miƙa mulki da karɓar aiki kafin ƙarshen aiki na ranar Alhamis, 23 ga Afrilu, 2026.
Comments
Post a Comment