Sanata Yayi Ya Fito Takarar Gwamnan Ogun
Sanata Solomon Adeola, wanda aka fi sani da Yayi, ya sanar da shiga takarar gwamnan Jihar Ogun a karkashin jam’iyyar APC domin zaben shekarar 2027.
Dan majalisar mai wakiltar yankin Ogun West ya sayi fom din tsayawa takara na jam’iyyar APC kan kudi har Naira miliyan 50 a birnin Abuja a yau.
Babban Sakataren Tsare-tsare na Kasa na jam’iyyar APC, Suleiman Argungu, ne ya mikawa wakilin Sanata Yayi takardun fom din a madadinsa.
Wannan mataki na nuna cewa Sanata Yayi ya fara shirin fafatawa a hukumance domin neman kujerar gwamnan jihar Ogun gabanin babban zaben shekarar 2027.
Comments
Post a Comment