Kabiru Marafa Ya Gana Da Shugabannin ADC A Abuja

Fitaccen ɗan siyasa kuma tsohon Sanata mai wakiltar Zamfara ta Tsakiya, Sanata Kabiru Garba Marafa, ya gana da shugabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar (ADC) daga Jihar Zamfara, a wani muhimmin taro da ya gudana a birnin Abuja..

Daga cikin mahalarta taron akwai Shugaban jam’iyyar ADC na Jihar Zamfara, Hon. Kabiru Garba Gusau, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar da suka halarta domin tattaunawa kan yiwuwar haɗin gwiwa a siyasa.

Rahotanni sun nuna cewa mahalarta taron sun yi cikakken nazari kan halin da siyasar Zamfara ke ciki a halin yanzu, tare da duba zabin dabaru da za su taimaka wajen gina wata sahihiyar dandalin siyasa da za ta iya samar da shugabanci nagari da ci gaba mai ɗorewa ga al’ummar jihar.

Majiyoyi sun ce wannan ganawa na daga cikin jerin tuntubar jam’iyyu daban-daban da Sanata Marafa ke yi, domin tantance wace jam’iyya ce za ta fi dacewa da manufofinsa na siyasa da kuma muradun al’ummar Zamfara.

Ana sa ran wannan mataki zai ƙara janyo hankalin jama’a yayin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa a sassan Najeriya, musamman a Jihar Zamfara, inda ake sa ido kan matakin da Kabiru Marafa zai ɗauka nan gaba.

Comments

Popular posts from this blog

BREAKING: FG Approves 40% Pay Rise —Non-Academic Staff Left Out

Nigeria’s Ivory Towers in Ruins: An Investigative Look at the Dilapidated State of Nigerian Universities

BREAKING: US Finally Withdraws from WHO