Sanatoci 9 Sun Fice Daga Jam’iyyunsu, Sun Koma Jam’iyyar ADC a Majalisar Dattawa

AA Tijjani
Wasu sanatoci tara na Majalisar Dattawan Najeriya sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyunsu na baya tare da komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a zaman majalisar da aka gudanar a ranar Alhamis.

Sanatocin da suka sauya sheƙa sun fito ne daga jam’iyyun Peoples Democratic Party (PDP), Labour Party (LP) da kuma All Progressives Grand Alliance (APGA).

Daga cikin sanatocin da suka koma ADC akwai Ireti Kingibe, wadda ke wakiltar Babban Birnin Tarayya, Abuja, (FCT) a Majalisar Dattawa, inda ta fice daga LP.

Haka kuma akwai Mohammed Ogoshi Onawo mai wakiltar Nasarawa ta Kudu wanda ya fice daga PDP, sai kuma tsohon gwamnan Jihar Sokoto kuma sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu Aminu Waziri Tambuwal, wanda shi ma ya sauya sheƙa daga PDP zuwa ADC.

Sauran sanatocin sun haɗa da Binos Dauda Yaroe (Adamawa ta Kudu, PDP), Austin Akobundu (Abia ta Tsakiya, PDP), da kuma Enyinnaya Abaribe (Abia ta Kudu, APGA).

Haka kuma akwai Victor Umeh (Anambra ta Tsakiya, LP), Tony Nwoye (Anambra ta Arewa, LP), da kuma Lawal Adamu Usman (Kaduna ta Tsakiya, PDP).

Rahotanni sun ce sanatocin sun sanar da sauya sheƙarsu ne a zauren Majalisar Dattawa, inda suka bayyana cewa sun yanke shawarar komawa ADC domin ci gaba da gudanar da siyasa bisa abin da suka kira sabon tsarin siyasa da zai inganta dimokuraɗiyya a ƙasar.

Sauya sheƙar sanatocin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da sauye-sauye a harkokin siyasar Najeriya, musamman yayin da jam’iyyun siyasa ke fara shirin tunkarar manyan zaɓuɓɓuka masu zuwa.

Masu sa ido kan harkokin siyasa na ganin cewa matakin na iya yin tasiri a daidaiton ƙarfi tsakanin jam’iyyun siyasa a Majalisar Dattawa.

Comments

Popular posts from this blog

BREAKING: FG Approves 40% Pay Rise —Non-Academic Staff Left Out

Nigeria’s Ivory Towers in Ruins: An Investigative Look at the Dilapidated State of Nigerian Universities

BREAKING: US Finally Withdraws from WHO