Da DUMI-DUMI: Ana Zargin Direban Motar Asibiti da Kashe Tsofaffi Biyar Yayin Kai Su Asibiti
Hukumomin birnin Forlì na Kasar Italiya sun kaddamar da bincike kan wani matashi mai shekaru 27 bayan mutuwar tsofaffi da dama a cikin motar asibiti da yake tukawa.
Wani lamari mai matuƙar tayar da hankali ya girgiza al’umma a ƙasar Italiya, bayan da hukumomin shari’a suka fara bincike kan wani direban motar asibiti mai shekaru 27 bisa zargin kashe akalla tsofaffi biyar yayin da yake jigilar su zuwa asibiti.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a birnin Forlì da ke arewacin ƙasar, inda ofishin mai gabatar da ƙara ya tabbatar da cewa an fara binciken ne bayan mutuwar wasu marasa lafiya da dama a cikin motar asibitin da direban ke aiki da ita.
A cewar jami’an bincike, mutanen da suka mutu dukkansu tsofaffi ne kuma suna fama da cututtuka daban-daban. Ana jigilar su ne daga gidajensu ko cibiyoyin kula da tsofaffi zuwa asibitoci domin duba lafiyarsu, amma sai suka rika mutuwa a hanya kafin su isa inda aka nufa.
Binciken farko ya nuna cewa tsakanin watan Fabrairu zuwa Nuwamba na shekarar 2025, mutane huɗu sun mutu yayin da ake jigilar su a motar asibitin da direban ke tukawa. Wannan ya sa kamfanin da yake aiki da shi ya fara zargin cewa akwai wani abu da ba daidai ba.
Saboda haka, kamfanin ya sanar da jami’an tsaro, inda aka fara sa ido na musamman kan motar asibitin. An kuma girka na’urorin ɗaukar bidiyo a cikin motar domin gano abin da ke faruwa yayin safarar marasa lafiya.
Bayan wannan mataki ne aka sake samun mutuwar wata tsohuwa mai shekaru 85 yayin da ake kai ta daga wani asibitin zuciya zuwa cibiyar kula da marasa lafiya. Rahotanni sun ce tsohuwar ta kamu da bugun zuciya ne a cikin motar asibitin kuma ta mutu kafin su isa inda aka nufa.
Binciken gawar da aka yi daga baya ne ya sa aka mika lamarin ga masu gabatar da ƙara domin zurfafa bincike kan yiwuwar aikata laifi.
Hukumomi sun bayyana cewa ana zargin direban na iya amfani da wasu hanyoyi ko sinadarai da ka iya haddasa mutuwar marasa lafiyan ba tare da an gane ba.
Sai dai lauyarsa ta bayyana cewa mutumin yana musanta dukkan zarge-zargen da ake masa, tana mai cewa yana cikin ruɗani kan yadda aka danganta shi da irin wannan mummunan laifi.
An dakatar da direban daga aiki yayin da bincike ke ci gaba, kuma jami’an shari’a sun ce idan aka tabbatar da zargin, zai iya fuskantar tuhume-tuhumen kisan kai ga mutane da dama, wanda hukuncinsa na iya zama mai tsanani a dokar ƙasar Italiya.
A halin yanzu dai hukumomi na ci gaba da tattara hujjoji domin gano gaskiyar abin da ya faru, yayin da lamarin ke jawo cece-kuce a cikin al’umma.
Comments
Post a Comment