🔥Ƴan Bindiga Sun Farmaki Amaechi, Sun Kona Ofishin Jam’iyya
Wasu Æ´an bindiga dauke da makamai sun kai mummunan hari kan ayarin motocin tsohon ministan sufuri a gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, wato Rotimi Amaechi, a jihar Rivers. Maharan sun kuma kona ofishin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) da ke garin Ubima.
Yadda harin ya faru
Rahotanni sun bayyana cewa Amaechi ya je garinsu Ubima da ke Æ™aramar hukumar Ikwerre ne domin yin rajistar zama É—an jam’iyyar ADC. Sai dai kafin zuwansa, wasu Æ´an bindiga sun mamaye yankin tare da kafa shinge a kan hanyar da ta haÉ—a Ubima da Omuanwa.
An ce maharan sun fara tayar da hankali tun daren Alhamis, inda suka kona ofishin jam’iyyar ADC na mazabar Ubima. Baya ga haka, sun yi ta harbe-harbe tare da lalata Æ™ofar gidan iyayen Amaechi ta hanyar harbin bindiga.
Majiyoyi sun ce manufar maharan ita ce tsoratar da magoya bayan Amaechi da kuma hana shi aiwatar da abin da ya zo yi a garin.
Jami’an tsaro sun fafata da maharan
Lokacin da ayarin motocin Amaechi ya isa inda Æ´an bindigar suka kafa shinge, jami’an tsaron da ke tare da shi sun gwabza musayar wuta da maharan.
A sakamakon hakan, jami’an tsaron sun fatattaki Æ´an bindigar zuwa cikin daji, inda suka tsere domin tsira daga harin.
Amaechi ya yi kira ga jami’an tsaro
Bayan ya ziyarci ofishin jam’iyyar da aka kona, Amaechi ya nuna godiyarsa ga jami’an tsaro, ciki har da kwamishinan Æ´an sanda, daraktan DSS da kuma kwamandan NSCDC na jihar Rivers saboda yadda suka kai masa dauki cikin gaggawa.
Ya kuma bukaci hukumomin tsaro su kamo wadanda suka kai harin domin a hukunta su bisa doka. Amaechi ya gargadi magoya bayansa da kada su dauki doka a hannunsu, yana mai cewa aikin jami’an tsaro ne su tabbatar da adalci.
Tsohon ministan ya kuma yi kira ga gwamnatin jihar Rivers da ta tabbatar da inganta tsaro domin kauce wa rikice-rikicen siyasa da ka iya jefa yankin cikin rashin zaman lafiya.
Comments
Post a Comment