Yanda Ƴan Bindiga Suka Kai Hari Masallaci a Kebbi, Suka Kashe Mutum Biyar
Rahoton NAN ya nuna cewa maharan sun afka wa masallacin ne yayin sallar magariba, inda suka bude wuta kan masu ibada.
Harin ya biyo bayan yunkurin kwanton bauna da suka yi wa ayarin wani babban hafsan sojin Najeriya mai mukamin Janar a kwanakin baya, wanda bai yi nasara ba – lamarin da ake ganin ya tayar musu da hankali.
Kakakin ’yan sandan jihar, SP Bashir Usman, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa harin na iya kasancewa ramuwar gayya bayan kaye da maharan suka sha a hannun sojoji.
Jami’an tsaro sun tsaurara matakan tsaro a yankin yayin da ake ci gaba da bincike.
Comments
Post a Comment