Amurka Za Ta Tura Sojoji 200 Zuwa Najeriya Don Taimakawa Yaki da Ƙungiyoyin Ta’addanci
Wannan mataki ya zo ne kwanaki kaɗan bayan Shugaba Donald Trump ya ba da umarnin kai hari ta sama kan wuraren da ake zargin mayakan Daesh/IS ke buya a yankunan Afrika.
Shirin ya ƙunshi horo da bayanan leken asiri
Rahotanni daga Amurka sun bayyana cewa sojojin da za a turo za su mayar da hankali ne kan:
- Horar da sojojin Najeriya a fagen yaƙi da ta’addanci
- Tallafin fasaha da dabarun yaƙi
- Raba bayanan leken siri
- Inganta haɗin guiwar rundunar ƙasa da ta sama
Hukumar tsaron Amurka ta tabbatar da cewa sojojin ba za su shiga yaƙi kai tsaye ba, illa dai su taimaka wajen shirye-shiryen tsaro da dabarun yaƙi. Rundunar sojin Najeriya ce za ta ci gaba da jagorantar dukkan hare-haren.
Dangantaka tsakanin Najeriya da Amurka ta ƙara ƙarfi
Masu sharhi sun yi nuni da cewa wannan tallafi na Amurka na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke fama da matsalolin tsaro masu yawa ciki har da:
- Hare-haren Boko Haram a Arewa maso Gabas
- Tashe-tashen hankulan ISWAP a yankin Tafkin Chadi
- Ƙara yawaitar hare-haren ’yan bindiga a Arewa maso Yamma
- Rikicin kabilanci da addini a wasu yankuna
Najeriya ta karyata zargin cewa tana nuna wariya wajen yaƙar kungiyoyin ta’addanci, tana mai cewa duk ’yan ta’adda ne ake nufi, ba tare da la’akari da addini ko kabila ba.
Amurka na ƙoƙarin faɗaɗa tasirinta a yaki da ta’addanci
Masu nazari sun ce wannan mataki na kara tura sojoji zuwa Najeriya na nuna yadda Amurka ke ƙara mayar da hankali kan Afrika, musamman bayan sabbin hare-haren da Trump ya dakatar, inda ya sha alwashin ƙara matsa lamba kan ƙungiyoyin da ke da alaƙa da ISIS.
A cewar jami’an tsaro, wannan haɗin gwiwa zai iya ƙara ƙarfin rundunar sojin Najeriya, tare da inganta dabarun yaƙi da amfani da bayanan sirri.
Comments
Post a Comment