🚨Takarar 2027 Zata Zama Ta Ƙarshe A Rayuwata — Inji Atiku Abubakar
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa zaÉ“en shugaban Æ™asa na shekarar 2027 zai kasance takararsa ta Æ™arshe a siyasar neman shugabancin Najeriya. 🗳️
Atiku ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise Television a ranar Laraba.
Ya tunatar da jama'a cewa ya fara neman kujerar shugaban ƙasa tun daga shekarar 1992, kuma ya shafe shekaru da dama yana fafutukar neman shugabanci a matakai daban-daban. Sai dai a wannan karon, ya ce idan ya sake tsayawa takara a 2027, wannan ne zai zama karshen gwagwarmayarsa ta neman shugabancin ƙasa.
Comments
Post a Comment