Masu Garkuwa Sun Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kisa Kan Mutane 176 da Suka Sace
Masu garkuwa da mutane da ake zargin ‘yan ta’addan Boko Haram ne sun bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin kwanaki guda domin biyan kuɗin fansa kan mutane 176, mafi yawansu mata da yara, da aka sace a ƙaramar hukumar Kaiama da ke jihar Kwara.
Rahotanni sun ce masu garkuwar sun nemi a biya Naira miliyan 20 kan kowane mutum, tare da yin barazanar kashe wasu daga cikin waɗanda suke tsare da su idan ba a biya kuɗin fansar cikin wa’adin da suka bayar ba.
Al’ummar yankin da iyalan wadanda abin ya shafa na kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta ɗaukar mataki domin ceto rayukan mutanen da aka sace.
Comments
Post a Comment