Jihohin Arewa 5 Za su Kasance Cikin Duhu Daga Afrilu 9 Zuwa Mayu 2 Inji Kamfanin Wutar Lantarki


Hukumar Hukumar Samar da Wutar Lantarki mai zaman kanta ta Najeriya (NISO) a taƙaice, ta sanar da al’ummarta a jihohin Adamawa, Gombe, Bauchi, Borno da Yobe cewa su shirya wa katsewar wutar lantarki a layin wutar Jos–Gombe 330kV daga ranar Alhamis 9 ga Afrilu zuwa 2 ga Mayu, 2026.

Sanarwar ta bayyana cewa katsewar wutar za ta riƙa faruwa ne domin ba da damar gudanar da gyaran manyan kayayyakin lantarki da sabunta tsarin sadarwa na wutar lantarki, wanda ake sa ran zai inganta samar da wuta a yankin bayan kammala aikin.

Jihohin da abin zai shafa: Adamawa, Gombe, Bauchi, Borno da Yobe

Lokacin katsewar: Daga 9:00 na safe zuwa 6:00 na yamma

Kwanakin katsewar: Daga Alhamis zuwa Lahadi a duk mako

Dalili: Gyara da sabunta layin wutar lantarki na Jos–Gombe 330kV

Hukumar NISO ta buƙaci al’umma da su yi haƙuri tare da ɗaukar matakan kariya, tana mai jaddada cewa aikin zai taimaka wajen inganta ɗorewa wutar lantarki da rage yawan matsalolin ɗaukewar wuta a nan gaba.

Comments

Popular posts from this blog

BREAKING: FG Approves 40% Pay Rise —Non-Academic Staff Left Out

Nigeria’s Ivory Towers in Ruins: An Investigative Look at the Dilapidated State of Nigerian Universities

BREAKING: US Finally Withdraws from WHO